وَأَلْقَتْ مَا فِيهَا وَتَخَلَّتْ ﴿٤﴾
Kuma ta jẽfar da abin da yake a cikinta, tã wõfinta daga kõme.
يَٰٓأَيُّهَا ٱلْإِنسَٰنُ إِنَّكَ كَادِحٌ إِلَىٰ رَبِّكَ كَدْحًۭا فَمُلَٰقِيهِ ﴿٦﴾
Ya kai mutum! Lalle ne kai mai aikin wahal da kai ne zuwa ga Ubangijinka, wahala mai tsanani, To, kai mai haɗuwa da Shi ne.
وَيَنقَلِبُ إِلَىٰٓ أَهْلِهِۦ مَسْرُورًۭا ﴿٩﴾
Kuma ya jũya zuwa ga iyãlinsa (a cikin Aljanna), yanã mai raha.
وَأَمَّا مَنْ أُوتِىَ كِتَٰبَهُۥ وَرَآءَ ظَهْرِهِۦ ﴿١٠﴾
Kuma amma wanda aka bai wa littãfinsa, daga wajen bãyansa.
إِنَّهُۥ كَانَ فِىٓ أَهْلِهِۦ مَسْرُورًا ﴿١٣﴾
Lal1e ne shi, yã kasance (a dũniya) cikin iyãlinsa yanã mai raha.
بَلَىٰٓ إِنَّ رَبَّهُۥ كَانَ بِهِۦ بَصِيرًۭا ﴿١٥﴾
Na'am! Lalle ne, Ubangijinsa Ya kasance Mai gani gare shi.
وَإِذَا قُرِئَ عَلَيْهِمُ ٱلْقُرْءَانُ لَا يَسْجُدُونَ ۩ ﴿٢١﴾
Kuma idan an karanta Alkur'ãni a kansu, bã su yin tawãli'u?